Ismail Khalif Shire, kwamandan runduna ta 60 ta sojojin Somalia, ya fadawa manema labarai cewa soja guda ya rasa ransa, wasu sojojin kuma sun samu raunuka a lokacin da suka yi arangama da mayakan a yankin Daynunay mai tazarar kilomita 30 daga garin Baidoa.
Shire ya ce, "mun kashe mayakan al-Shabab 8 da jikkata wasu da dama, mun tarwatsa mayakan, mun kwace yankin, sannan mun kwaso gawawwakin su zuwa wannan wajen".
Sai dai mayakan al-Shabab sun yi ikararin kwace ikon yankin Daynunay tare kwato makamai daga sansanin sojojin.
Fadan na baya bayan nan ya zo ne kwanaki 2 bayan da mayakan al-Shabab suka kaddamar da harin kunar bakin wake a ranar Asabar lamarin da yayi sanadiyyar rayukan mutane 22 da raunata wasu 36 a garin Baidoa dake shiyyar Bay. (Ahmad)