in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a tagwayen harin kunar bakin wake ya karu a Somalia
2018-10-14 15:48:36 cri
Jami'ai a Somaliya sun ce adadin mutanen da suka mutu a sanadiyyar tagwarin harin kunar bakin wake a garin Baidoa dake kudancin Somaliya ya karu zuwa mutane 10.

Ugas Hassan Abdi, ministan yada labarai na jahar kudu maso yammacin kasar ya ce, a kalla mutane 10 ne suka mutu, kana wasu sama da 20 kuma suka jikkata a harin. Mafi yawan wadanda suka mutu fararen hula ne, in ji ministan.

Wadanda suka mutu, galibinsu matasa ne, da suka taru domin shan shayi a lokacin da dan kunar bakin waken ya kaddamar da harin inda ya hallaka kansa nan take a wani gidan sayar da abinci kana mintoci kadan bayan harin farko, aka sake kaddamar da wani harin a otel din Bilan dake tsakiyar garin.

Abdifitah Muhidin, wanda ya ganewa idonsa faruwar lamarin, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, ya ga gawawwakin mutane da dama kwance a kasa bayan kaddamar da harin.

Kungiyar mayakan al-Shabab ta dauki alhakin kai harin, ta ce mayakanta ne suka kashe sama da mutane 20. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China