in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyi 27 ne daga Afrika ta kudu za su halarci bikin baje kolin shigo da kayayyaki zuwa kasar Sin
2018-11-05 11:01:00 cri
Kimanin kungiyoyi 27 daga kasar Afrika ta kudu ne ake sa ran za su halarci bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin (CIIE) na kasa da kasa wanda aka bude a yau Litinin, kamar yadda sashen kula da ciniki da masana'antun kasar (DTI) ya sanar a jiya Lahadi.

Kungiyoyin sun hada da na sarrafa kayan amfanin gona, da na hada takalman fata, da kere kere, da sinadaran albarkatun man fetur, da kayayyakin jiragen kasa, da kayayyakin tsaro, da fasahar sadarwa ta zamani da dai sauransu, inda za su halarci tarurruka daban daban domin tallata kayayyakin da kasar ke samarwa da kuma neman hanyoyin zuba jari.

"Babban abin da za'a mayar da hankali shi ne yadda za'a ja hankalin masu sha'awar zuba jari da masu sayen kayayyakin da kasar Afrika ta kudu ta sarrafa," in ji kakakin hukumar DTI Sidwell Medupe.

Ministan ciniki da masana'antun kasar Afrika ta kudu Rob Davies, shi ne zai jagoranci tawagar wakilan kasar wanda zai gabatar da jawabi a taron dandalin zuba jari na kasar Afrika ta kudu a yayin bikin baje kolin na CIIE. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China