in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankunan kasar Kenya za su halarci bikin CIIE
2018-11-02 11:15:29 cri
Kwanaki kalilan suka rage a kaddamar da bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin (CIIE) karo na farko a birnin Shanghai na kasar. Kasancewarsa banki mafi girma a gabashin nahiyar Afirka, bankin kasuwancin kasar Kenya zai halarci bikin. Babban darektan bankin, Reginald Kikwai ya ce, a halin yanzu, Kenya na harkokin cinikayya da kasar Sin, don haka, kamfanonin Kenya da na kasar Sin da ke gudanar da harkokinsu a kasar Kenya, dukkansu na bukatar hidimomin hada-hadar kudi. Yana mai fatan bikin baje kolin da za a gudanar zai taimaka ga kyautata tasirin bankin.

Sai dai duk da saurin karuwar harkokin cinikayya tsakanin Sin da Kenya, kasashen biyu na fuskantar matsalar rashin daidaiton ciniki. Game da wannan, Kikwai ya ce, taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a birnin Beijing ya nuna cewa, kasar Sin za ta habaka shigo da kayayyaki daga kasashen Afirka, don haka, kara shigo da kayayyaki daga kasashen Afirka zai zama sabon bangaren da sassan biyu za su mai da hankali a kai a hadin gwiwarsu. Ya ce, "a sabo da haka ne, wasu kamfanonin kasar Kenya za su halarci bikin, kuma a lokacin da suke ciniki, bankin kasuwancin kasar Kenya zai iya kasancewa kyakkyawan abokin hadin gwiwa a gare su." (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China