in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin zai samar da damarmakin kasuwanci ga kasashen Afrika
2018-11-04 15:26:14 cri
Bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin na kasa da kasa, wanda zai gudana a Shaghai daga ranar 5 zuwa 10 ga wata, zai bude kofofin kasuwanci da dama ga kasar Afrika ta kudu da ma nahiyar Afrika baki daya.

Wannan shi ne ra'ayin galibin 'yan kasuwa da kamfanoni da masu sharhi kan al'amuran ci gaba na Afrika ta kudu da suka gana da kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Wani mai sharhi kan harkokin ci gaba a kasar Afrika ta kudu Ruben Richards, ya ce bikin zai bada damar jure yanayin rashin tabbas da tattalin arziki ke ciki.

Ruben Richards wanda shi ne shugaban gidauniyar Ruben Richards, kuma tsohon sakataren zartarwa na hukumar warware sabani ta Afrika ta kudu, ya ce wannan dama ce ta musamman da za a gwada kayayyakin kasarsa a babbar kasuwa da kuma yanayin tattalin arziki mai sarkakiya.

Ita kuwa shugabar cibiyar kasuwanci da masana'antu ta Cape, Janine Myburgh, shawartar 'yan kasuwa masu fitar da kayayyaki ta yi, da su rika shiga bukukuwa irin wannan, domin yana bada kyawawan damarmakin haduwa da masu sayayya da kuma gano damarmaki ko gibi a kasuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China