in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bikin baje kolin CIIE ya shaida niyyar gwamnatin kasar Sin na bude kofarta ga duniya, in ji jami'in Kenya
2018-10-31 13:47:03 cri
Shugaban sashen kula da harkokin kasashen Asiya da Australia Christopher Chika a jiya Talata ya bayyana cewa, bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin wato CIIE a takaice, wanda za a kaddamar a karo na farko ya shaida niyyar gwamnatin kasar ta Sin ta bude kofarta ga kasuwannin kasashen duniya, kuma gwamnatin Kenya na son kulla yarjejeniyoyi tare da kasar Sin, don sa kaimin shigar da amfanin gonar kasar zuwa kasuwannin kasar Sin.

A gun taron shawarwari da aka gudanar a wannan rana a ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Kenya, Mr. Christopher Chika ya bayyana cewa, "A ganina, kasashen Afirka musamman ma Kenya na bukatar wannan bikin baje kolin. Muna shirin kafa wani gidan nune-nune na kayayyakin Kenya, don nuna kayayyakin da muke son fitarwa zuwa kasar Sin."

Jami'in ya kara da cewa, shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta zai halarci bikin, don kaddamar da gidan nune-nunen kayayyakin kasar Kenya. A sa'i daya kuma, akwai kamfanoni masu zaman kansu kimanin tara da suka yi rajistar halartar bikin. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China