in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Zimbabwe na fatan kara fahimtar kasuwar kasar Sin ta hanyar halartar taron CIIE
2018-11-01 10:54:39 cri
A kwanakin baya ne, ministan kula da harkokin masana'antu da kasuwanci na kasar Zimbabwe Mangaliso Ndlovu ya bayyana cewa, kasarsa na matukar son fadada hanyoyin shiga cikin kasuwannin kasar Sin ta hanyar halartar bikin baje-kolin kayayyakin kasa da kasa da ake shigowa da su kasar Sin karo na farko wato CIIE a takaice, wanda za'a yi a watan Nuwamban bana.

Yayin da yake amsa tambayoyin 'yan jaridu, Mangaliso Ndlovu ya ce, kamfanonin Zimbabwe ba su shiga cikin kasuwannin kasar Sin sosai ba. A wajen taron koli na Beijing, na dandalin tattauna hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya baiwa kamfanonin Afirka kwarin-gwiwar shiga cikin kasuwannin kasar Sin, al'amarin da ministan ya ce ya karfafa musu gwiwa sosai. Mangaliso Ndlovu, ya kara da cewa yana fatan yin amfani da wannan dama wajen kara fahimtar hajjojin da masu sayayyar kasar Sin suke sha'awa da ma'aunin hajjojin kasar, ta yadda za su kara shiga cikin kasuwannin kasar ta Sin.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China