in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta damu da karuwar adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2018-11-02 10:27:30 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce ta damu da karuwar adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo cikin makonni 4 da suka gabata, duk da gagarumin ci gaba da aka samu ta fuskar daukar matakan tunkarar cutar.

Wata kiddiga ta baya-bayan nan da hukumar ta fitar, ta ce ya zuwa ranar Talata, akwai mutane 279 da aka yi wa rejistar cutar Ebola, da suka hada da wadanda aka tabbatar sun kamu da ita 244 da kuma wadanada ake kyautata zaton sun kamu guda 35, yayin da adadin wadanda suka mutu ya karu zuwa 179. Dukkan wadannan adadi an same su ne a lardin arewacin Kivu dake makotaka da lardin Ituri.

WHO ta yi gargadin cewa, bisa yanayin da ake ciki, har yanzu barazanar yaduwar cutar zuwa wasu lardunan kasar da kuma kasashe makwabta na da yawa.

Ta kara da cewa, yayin da take bibiyar yanayin barkewar cutar, nazarinta kan barazanar yaduwar cutar Ebola bai sauya ba, wanda ke nufi matakin a kasar da yankin na sama sosai, yayin da yake kasa a duniya.

Hukumar ta ci gaba da bada shawarar kada a haramta ziyarta ko cinikayya da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo saboda wadannan bayanai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China