in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
RD-Congo: 'Yan adawa sun sanar da yin zanga zanga domin tilasta gudanar da zabuka bisa wa'adin kudin tsarin mulki
2016-05-14 11:46:04 cri
Wasu kungiyoyi mambobin kawancen 'yan adawa na jamhuriyar demokaradiyar Congo, musamman G7 da gamayyar kishin kasa, sun bayyana a ranar Jumma'a fara ayyukan zanga-zanga na gama gari a dukkan fadin kasar domin tilasta gudanar da zabuka bisa wa'adin kundin tsarin mulkin kasa. Hakan ya biyo bayan wata sanarwar siyasa da suka yi a birnin Kinshasa inda shugabannin adawar suka jaddada kin amincewarsu na ganin shugaba Joseph Kabila ya ci gaba da tsayawa kan mulkin bayan wa'adinsa dalilin rashin gudanar da zabuka a wannan shekara kamar yadda alkalan kotun kolin kasar suka bayyana. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China