in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 40 ne 'yan tawayen ADF suka kashe a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2017-10-09 09:22:42 cri
Wata majiya daga rundunar sojin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta ce 'yan tawayen ADF su yi mutane a kalla 40 kisan kiyashi a yankin Beni na lardin arewacin Kivu dake gabashin kasar.

Majiyar ta ce 'yan tawayen sun kuma kai hari kan sansanonin soji daban-daban dake Beni.

Wadanda suka tsira daga hare-haren, sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, sai da 'yan tawayen suka saki wasu mutane daga cikin wadanda suka kama kafin daga bisani su kashe sauran.

Hukumomin soji sun bayyana cewa, har yanzu dai ana zaman fargaba a yankin

Gwamnatin Uganda ta dauki kungiyar ADF a matsayin ta ta'addanci. Tun asali, kungiyar ta kasance ne a yammacin Uganda kafin daga bisani ta fadada zuwa Jamhuriyar Demokradiyyar Congo dake makwabtaka da kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China