in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO: An fara allurar riga kafin Ebola a jamhuriyar dimokuradiyyar Congo
2018-08-09 20:31:22 cri
Jami'an lafiya a lardin Arewacin Kivu na jamhuriyar dimokuradiyyar Congo, sun fara gudanar da alluran rigakafin cutar Ebola mai saurin kisa.

Rahotanni daga hukumar lafiya ta duniya WHO sun bayyana cewa, an fara gudanar da rigakafin ne a yankuna da suka fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar. An kuma fara da yi wa ministan lardin, da jami'in tsare tsaren aikin rigakafin wannan allura, a aikin da ake fatan fadada shi, ta yadda dukkanin wadanda suka dace a yi musu allurar za su amfana. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China