in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shirin wanzar da zaman lafiya na AU ya musanta rahoton kashe sojojinsa 30 a Somaliya
2018-10-31 11:22:56 cri
Shirin kiyaye zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika a Somaliya (AMISOM), a jiya Talata ya karyata rahotannin dake cewa mayakan al-Shabab sun kashe sojojin AMISOM 30 a wani harin da suka kaddamar kan tawagar sojojin a yankin Hiraan dake tsakiyar Somaliya a ranar Litinin

A wata sanarwar da hukumar ta AU ta fitar, ta musanta rahotannin, inda ta ce karya ce kawai aka kitsa da nufin kawar da hankulan jama'a daga ayyukan da dakarun tsaron suke yi a kokarinsu na murkushe mayakan al-Shabab, wanda dakarun na AU tare da jami'an tsaron kasar Somaliya ke gudanarwa bisa hadin gwiwa.

A ranar Litinin ne kungiyar 'yan ta'addan ta yi ikirarin hallaka sojojin kasar Habasha 30, wadnda ke aiki karkashin dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika wanda ta ce ta hallaka su a wani harin bam a yankin Hiraan.

Wasu boma bomai da aka dana a gefen hanya da ake sarrafa su da na'ura ne suka tashi da wasu tawagar jami'an tsaron a lokacin da suke kan hanyarsu daga BeletWeyne zuwa Kalabeyr a kusa da kan iyakar Somaliya da Habasha. Al-Shabab ta ce, abubuwan fashewa sun lalata motocin jami'an tsaron, inda kuma suka hallaka sojojin nan take.

Sai dai kuma, AMISOM ta ce sojojinta 4 ne kawai suka samu kananan raunuka, kuma ana ba su kulawa a wani asibiti dake kusa da yankin Beletweyene. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China