in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta jinjinawa Habasha sakamakon sassauta ka'idojin biza ga matafiyan Afrika
2018-10-12 10:48:14 cri
Kungiyar tarayyar Afrika (AU) a jiya Alhamis ta yabawa kasar Habasha saboda sanarwar data bayar na saukaka takardun izinin shiga kasar wato biza ga 'yan kasashen Afrika da suke son yin bulaguro zuwa kasar ta gabashin Afrika.

A jawabin da ya gabatar a taron hadin gwiwar majalisun dokokin kasar Habasha a ranar Litinin, shugaban kasar Habashan Mulatu Teshome, ya sanar cewa, kasarsa zata bullo da sabon tsarin bada biza ga dukkan mutanen dake dauke da takardun fasfo na kasashen Afrika da suke muradin shiga kasar, kana matakin zai fara aiki ne tun a shekarar 2018/19.

Da yake yin maraba da matakin da Habashan ta dauka, shugaban gudanarwar kungiyar AU, Moussa Faki Mahamat, ya yabawa dukkan kasashen mambobin kungiyar AU wadanda suka riga suka dauki matakan saukaka tsarin tafiye tafiye a tsakanin 'yan kasashen nahiyar ta Afrika.

Faki, ya bukaci dukkan kasashen mambobin kungiyar wadanda har yanzu basu aiwatar da wannan tsari ba dasu hanzarta daukar wannan mataki, kamar yadda wata sanarwa da AU ta fitar a ranar Laraba ta tabbatar da hakan. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China