in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birtaniya ta yi gargadi game da gaggawar ficewar dakarun AU daga Somalia
2018-10-08 10:09:07 cri
Ministar gwamnatin Birtaniya mai lura da harkokin da suka jibanci nahiyar Afirka Harriett Baldwin, ta yi gargadin cewa, gaggauta ficewar dakarun wanzar da zaman lafiya, na kungiyar hadin kan Afirka AU daga kasar Somalia, na iya haifar da mummunan sakamako.

Harriett Baldwin, ta ce maimakon maida hankali ga wani wa'adi na aikin tawagar, ya fi dacewa a maida hankali ga yanayin da kasar ke ciki, sa'an nan a janye dakarun sannu a hankali, gwargwadon karfin ikon tafiyar da tsaron kasar, da sojoji da sauran jami'an tsaron kasar ke da shi.

Wata sanarwa da tawagar AMISOM ta fitar a ranar Lahadi, ta rawaito Baldwin na cewa, har kullum Birtaniya na jaddada muhimmancin janye tawagar AMISOM bisa ikon dakarun soji da 'yan sandan kasar Somaliyar na kare kasar. Ta ce hakan shi ne mafi muhimmanci, ba wai wani wa'adi da aka tsara kan wani jadawali ba.

Ministar wadda ta ziyarci birnin Mogadishu a ranar Asabar, ta yabawa dakarun wanzar da zaman lafiya dake aiki karkashin tawagar AMISOM, ta na mai cewa kasar ta za ta ci gaba da nemawa tawagar cikakken goyon bayan kasashen duniya, a fannin samar da kudaden gudanar da ayyukan ta. (Fa'iza Mustafa)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China