in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya yi kira da a ci gaba da bada agajin jin kai ga al'ummar Syria
2018-10-30 09:31:48 cri
Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya yi kira ga al'ummomin kasa da kasa su ci gaba da samar da kayayyakin jin kai domin taimakawa al'ummar Syria dake cikin bukata.

Jami'in ya yi wannan kira ne yayin taron kwamitin sulhu na MDD da aka yi kan yanayin da Syria ke ciki.

Ya kara da cewa, akwai bukatar taimakawa kokarin gwamnati da al'umma na sake gina kasar, yana mai cewa ya kamata kasashen duniya su marawa gwamnatin kasar baya a kokarin da take na samar da kayayyakin jin kai ga fararen hula dake cikin mawuyacin hali tare da kara tsayuwar daka wajen yaki da barazanar ta'addanci a kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China