in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta gabatar da na'urorin sarrafa wutar lantarki ga gwamnatin Syria
2018-10-11 10:35:01 cri
Gwamnatin kasar Sin ta gabatar da na'urorin sarrafa wutar lantarki 800, da wasu manyan wayoyin lantarki ga gwamnatin Syria, a matsayin tallafin sake ginin kasar da yaki ya daidaita. Bayan isar kayan tallafin a 'yan kwanakin baya, an gabatar da bikin mika su ga mahukuntan Syria a wannan rana.

Da yake tsokaci ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua game da hakan, jami'i a ofishin jakadancin Sin dake birnin Damascus Ma Xuliang, ya ce wannan tallafi zai yi tasirin gaske, wajen farfado da yanayin zamantakewar al'ummar Syria, da kyautata ababen more rayuwar su, da kuma inganta fannin samar da hidima.

Jami'in ya kuma jaddada cewa, tallafin na baya bayan nan, na cikin jerin taimako da Sin ke gabatarwa, don ba da gudummawa wajen sake ginin kasar ta Syria. Ya ce a nan gaba, Sin za ta ci gaba da samar da tallafin jin kai ga kasar.

Shi kuwa a nasa bangaren, mataimakin ministan ma'aikatar lantarki ta kasar Syria Nidal Qarmoushi, ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, taimakon kayayyakin samar da lantarki na Sin, ya zo ne a daidai gabar da ake matukar bukatar sake gina ababen more rayuwa a kasar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China