in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin mahajjantan Masar da suka rasu ya karu zuwa 70
2018-09-11 10:04:43 cri
Ma'aikatar lafiya ta kasar Masar, ta ce jimilar mahajjatan kasar 70 ne suka rasu yayin aikin hajjin bana da aka kammala a makon karshe na watan Augusta.

Sanarwar da kakakin ma'aikatar Khaled Megahed ya fitar, ta ce rahoton baya-bayan nan na nuni da cewa, mahajjata biyu sun mutu sanadiyyar matsananciyar ciwon zuciya da na numfashi.

Ya kara da cewa, hukumomin kasar na aiki da takwarorinsu na Saudiyya domin samun takardar shaidar mutuwar mahajjatan.

Mace-mace sanadiyyar zafi da gajiya da sauran wasu abubuwa indallahi, abu ne da aka saba gani yayin aikin hajji a Saudiyya.

Sama da mahajjata 84,000 'yan kasar Masar ne suka sauke farali bana, inda jimilar al'ummar duniya da suka yi aikin hajjin ya kai miliyan 2.4.

A bara, sama da mahajjatan Masar 80 ne suka mutu daga cikin mahajjata 70,000. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China