in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yankewa wasu kusoshin kungiyar 'yan uwa musulmi ta Masar hukunci
2018-08-13 10:40:49 cri
Wata kotu dake zamanta a birnin Giza dake Masar ta yankewa wasu kusoshin haramtacciyar kungiyar nan ta 'yan uwa musulmi su 5 hukuncin daurin shekaru 25, bisa samun su da laifin tunzura zanga zanga, da kitsa tashin hankali da kisan fararen hula. Cikin mutanen 5 da aka yankewa hukuncin hadda daya daga jagororin kungiyar Mohamed badie.

Kotun ta kuma yankewa tsohon minista a fambararriyar gwamnatin Mohamed Morsi, wato Bassem Ouda, hukuncin daurin shekaru 15, yayin da ta kuma zartas da hukuncin daurin shekaru 10 ga wasu mutane su 3. To sai dai kuma ana iya daukaka kara game da wannan hukunci.

Hukuncin ya biyo baya na shari'ar da aka sabunta kan mutanen, bayan da a watan Satumba na shekarar 2014, kotun ta yankewa wasu magoya bayan kungiyar su 15 hukuncin daurin rai da rai.

A wani ci gaban kuma, wata kotun dake zaman ta a birnin Alkahira, ta mika takardun neman amincewar babban mai bada fatawa na kasar, game da yiwuwar zartas da hukuncin kisa kan wasu 'yan kungiyar su 3 da ake tsare da su, bayan da ta tabbatar da zargin da ake musu na kafa kungiya mai adawa da gwamnatin kasar ta Masar, da kuma goyon bayan ta'addanci. Ana dai sa ran kotun za ta bayyana hukuncin karshe kan mutanen su 3 a ranar 14 ga watan Oktoba dake tafe. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China