in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ba ta samu bakin haure ba tun daga shekarar 2016
2018-09-17 10:45:18 cri
Shugaban Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya ce kasarsa ba ta samu bakin haure ba tun daga 2016.

Shugaba al-Sisi na bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da shugaban Majalisar Tarayyar Turai Donald Tusk da shugaban gwamnatin Austria, Sebastia Kurz dake ziyara a Masar.

Sanarwar da fadar shugaban Masar ta fitar, ta ruwaito shugaban ya kuma bayyana kokarin kasarsa na yaki da kwararar bakin haure da kare iyakokinta na kasa da na ruwa, yayin da ake tsaka da fama da rashin tsaro a kasashen dake makwabtaka da ita.

Sanarwar ta ce Abdel-Fattah al-Sisi da bakin nasa, sun kuma tattauna kan halin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya, musammam Libya da Syria, inda ta ce dukkansu sun amince cewa maslahar siyasa ce za ta kawo karshen rikicin da kwararar bakin haure.

A baya, Masar ta kasance inda bakin haure ke bi don tsallakawa zuwa Libya akan hanyarsu ta zuwa Turai ta tekun Bahar Rum. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China