in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta alkawarta goyon baya ga sabbin ministocin da aka nada a Libya
2018-10-08 13:32:23 cri
Tawagar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya a Libya ko UNSMIL a takaice, ta bayyana goyon bayan ta, ga sabbin ministocin da firaministan Libiya Fayez Serraj ya nada a ranar Lahadi. Baya ga ministocin guda 3, firaminista Serraj, ya kuma nada shugaban babbar hukumar wasanni da harkokin matasa ta kasar.

Cikin wani sakon taya murna ta shafin tweeter, ofishin UNSMIL ya taya sabbin wadanda aka nada din karkashin gwamnatin hadin kan kasa ta GNA murna, tare da fatan samun cikakken goyon bayan MDDr.

Kaza lika ofishin ya ce zai ci gaba da tallafawa ministocin, wajen aiwatar da sabbin matakan tsaro a birnin Tripoli, da fadada matakan sauya tsarin tattalin arzikin kasar, da kuma samar da daidaito a tsakanin hukumomin kasar. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China