in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyya mai mulki a Aljeriya ta tsayar da Bouteflika takarar shugabancin kasa a zaben 2019
2018-10-29 09:16:48 cri
Jam'iyya mai mulki a kasar Aljeriya ta sanar a jiya Lahadi cewa shugaban kasar mai ci Abdelaziz Bouteflika shi ne dan takara daya tilo da zai tsayawa jam'iyyar a zaben shugaban kasar da za'a gudanar a watan Afrilun shekarar 2019, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar APS ya sanar.

"Bouteflika shi ne shugaban kasa kuma shugaban jam'iyyar. Ba mu da wani sauran dan takara a zaben shugaban kasar na shekarar 2019 sai Bouteflika," sakatare janar na jam'iyyar NLF mai mulkin Djamel Ould Abbas ne ya bayyana hakan.

Bouteflika, mai shekaru 81, yana fama da matsalolin rashin koshin lafiya bayan da ya kamu da cutar shanyewar jiki a shekarar 2013, tun daga wancan lokacin ya rage yawan fitowa a bainar jama'a.

An sake zabarsa a shekarar 2014 a wa'adin mulki karo na 4 wanda zai kare a shekarar 2019, Bouteflika wanda ake sa ran zai nemi wa'adin mulki a karo 5 matukar kundin tsarin mulkin kasar ya lamince masa, kamar yadda wasu masu sanya ido suka bayyana. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China