in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeria za ta karbi bakuncin taron yaki da ta'addanci a watan Afrilu
2018-03-12 10:49:47 cri
Ministan harkokin wajen Aljeria Abdelkader Messahel, ya sanar da cewa kasarsa za ta karbi bakuncin babban taro kan yaki da ta'adanci da samarwa 'yan ta'adda kudi a watan Afrilu mai zuwa.

Biyo bayan ganawar da ya yi da shugaban hukumar AU Musa Faki Mahamat dake ziyara a Algiers, Messahel ya shaidawa manema labarai cewa, taron zai gudana ne a ranar 9 ga watan Afrilu, inda ya ce tuni ya samu sahalewar kwamitin sulhu na AU a watan Satumban 2014, domin inganta hadin kai wajen yaki da ta'addanci a tsakanin kasashen Afrika.

Abdelkader Messahel ya kara da cewa, taron na da matukar muhimmanci la'akari da yanayin da ake ciki a yanzu, domin zai bada dama ta musayar ra'ayi kan dokokin yaki da ta'addanci a kasashe mambobin AU da kuma cimma matsaya daya a tsakaninsu a wannan bangare.

Har ila yau, ya ce taron na da nufin bayyana rawar da hukumomin nahiyar Afrika ke takawa a fannonin yaki da ta'addanci da halasta kudin haram da fasa kauri da sauran laifuka. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China