in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya za ta karbi bakuncin taron OPEC a watan Satumba
2018-07-13 10:05:24 cri
Ministan makamashi na kasar Aljeriya Mutapha Guitouni ya bayyanan cewa, kasarsa za ta karbi bakuncin taron kasashe masu arzikin hako man fetur (OPEC) a karshen watan Satumban wannan shekara.

Ministan wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a Algiers, babban birnin kasar, ya ce taron zai baiwa kasashen kungiyar ta OPEC damar hada kai don tattauna yadda za a daidaita farashin man a kasuwannin duniya.

Ya ce, farashin man ya tashi, saboda wasu dalilai na kasuwa, amma komai zai daidaita bayan an cimma daidaito kan yadda ake samar da man da kuma bukatarsa.

Ya kuma yi nuni da cewa, yarjejeniyar da aka cimma a watan Disamban shekarar 2016 tsakani kasashen kungiyar da wadanda ba sa cikin kungiyar, kamar kasar Rasha, kan yadda za a janye ganga miliyan 1.8 a kowa ce rana daga kasuwa, matakin ya taimaka wajen daga farashin man tsakanin dala 70 zuwa 80 kan kowace ganga.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China