in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mayakan Boko Haram sun hallaka jami'ar Red Cross
2018-10-16 19:18:58 cri
Gwamnatin Najeriya ta ce kungiyar 'yan ta'adda ta Boko Haram, ta hallaka Hauwa Mohammed, jami'ar lafiya mai aiki da kungiyar ba da agajin jin kai da kasa da kasa ta Red Cross.

Wata sanarwar da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua ya samu kwafin ta a birnin Lagos, ta rawaito ministan watsa labarai da raya al'adu na kasar Lai Mohammed, na ce gwamnatin kasar ta kadu matuka, da samun labarin kisan jami'ar ta Red Cross, duk kuwa da matakan da gwamnati ta dauka na kaucewa hakan, da ma kiraye kiraye da aka yi ta yi daga sassa daban daban, na ganin matashiyar ta tsira da ranta. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China