in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD na fatan Rasha da Amurka za su warware sabanin dake tsakaninsu game da yarjejeniyar makaman nukiliya
2018-10-23 10:57:14 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya bayyana fatan Rasha da Amurka, za su warware sabanin da suka samu game da sanarwar da Amurka ta yi na shirin janyewa daga yarjejeniyar hana amfani da makami mai linzami na nukiliya mai cin gajere da matsakaicin zango.

Yayin da yake bayani game da jawabin Sakatare Janar din a jiya, mataimakin kakakin majalisar Farhan Haq, ya tunatar cewa, cikin jawabi da ya yi a jami'ar Geneva a watan Mayun da ya gabata, Antonio Guterres, ya yi kira ga gwamnatin Rasha da ta Amurka, su warware sabanin dake tsakaninsu dangane da yarjejeniyar.

A karshen makon da ya gabata ne, shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa, zai janye daga yarjejeniyar da aka cimma a shekarar 1987 tsakanin shugaban kasar Amurka na wancan lokaci Ronald Reagan da Jagoran Tarayyar Soviet Mikhail Gorbachev, wadda ta haramtawa kasashen biyu mallaka da kerawa da kuma gwajin makami mai linzami mai cin kilomita 500-5,500.

Bayan sanarwar da shugaba Trump ya yi ne mataimakin ministan harkokin wajen Rasha Sergei Ryabkov ya bayyana irin wannan yunkuri a matsayin mai hadarin gaske.

Kamfanin dillancin labarai na kasar TASS, ya kuma ruwaito shi yana gargadin cewa, matakin zai iya janyo kakkausar suka daga al'ummomin duniya da suka jajirce wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China