in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci a kyautata hanyoyin tattara kudaden ayyukan MDD
2018-10-11 09:46:24 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD ya bukaci a kara mayar da hankali game da batun tattara kudaden da MDD ke gudanar da ayyukanta.

"A halin yanzu hukumar tana fama da manyan kalubaloli na karancin kudade wanda yana bukatar dukkan bangarorin da abin ya shafa su sa kai wajen sauke nauyin dake wuyansu ta hanyar bada gudumawarsu," in ji Ma Zhaoxu zaunannen wakilin Sin a MDD yayin da ya bayyana hakan a taron kwamitin gudanar da kasafin kudi na MDD karo 5 a ranar Talata.

Ma ya ce, akwai kura kurai da ake tafkawa wajen yadda ake tantance kason kudaden da kowace kasa za ta bayar bisa la'akari da banbancin dake tsakanin kasashen da suka ci gaba da kasashe masu tasowa..

Game da batun kiyasin ayyukan wanzar da zaman lafiya kuwa, kasar Sin tana goyon bayan a gudanar da ayyukan hadin gwiwa da daukar nauyi ayyuka na musamman, in ji jakadan na Sin.

Duk da bunkasuwar tattalin arzikin da take samu, "kasar Sin har yanzu kasa ce mai tasowa idan aka yi la'akari da ma'aunin kudaden shigar jama'ar kasar wanda yake a matsayi na 70 a duniya," jakadan ya nanata cewa, kasar Sin za ta kara tallafinta wajen shirin wanzar da zaman lafiya nan MDD daga shekarar 2019-2021. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China