in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang: kasar Sin za ta kara sassauta sharudan shigar da baki 'yan kasuwa kasar
2018-10-17 11:26:49 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang wanda ya yi ziyara a kasar Holland, da takwaransa na kasar Mark Rutte, sun halarci wani taron kara wa juna sani da masu tafiyar da masana'antun kasar, a birnin Hague, jiya da rana, agogon wurin.

Bayan ya saurari jawaban da masu masana'antu suka bayar bi da bi, Li Keqiang ya bayyana cewa, kasar Sin za ta samar da karin damamaki ga baki 'yan kasuwa wadanda suke da shirin zuba jari a kasar, sannan za ta kara sassauta sharudan shigar da su kasuwar kasar Sin. Dukkan masana'antun da za su yi rajista a kasar Sin, za su samu matsayi iri daya da na masana'antun kasar. Bugu da kari, kasar Sin za ta dauki kwararan matakan kare ikon mallakar fasaha, kana ba za a amince da tilastawa wani mika fasaharsa zuwa ga wani daban ba.

Bayan taron, Li Keqiang da Mark Rutte sun halarci wani bikin kulla wasu yarjejeniyoyin hadin gwiwa tsakanin masana'antu da kamfanonin kasashen biyu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China