in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya isa Brussels domin halartar taron shugabannin kasashen Asiya da Turai karo na 12
2018-10-17 09:47:13 cri
Firaminista Li Keqiang na kasar Sin, ya isa birnin Brussels na kasar Belgium jiya Talata da dare, agogon wurin, domin ziyarar aiki da halartar taron shugabannin kasashen Asiya da Turai karo na 12, bisa gayyatar da Donald Tusk‎, shugaban kwamitin majalisar Turai da Mr. Jean –Claud Juncke, shugaban kwamitin kungiyar EU da kuma firaminista Charles Michel na kasar Belgium suka yi masa.

Li Keqiang ya bayyana cewa, halin rashin tabbas da ake ciki yanzu a duniya na cike da sarkakiya, amma tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwa da bude kofa tare da hadin gwiwa, hanzu yanzu, su ne manyan jigon dake kasancewa a wannan zamanin. Ya ce ya kamata nahiyoyin Asiya da Turai, wadanda suke kasancewa muhimman karfi ga kokarin ci gaban tattalin arziki da tabbatar da kwanciyar hankalin duniya, su kara yin mu'amala da hadin gwiwa, ta yadda za su iya yin kokarin tabbatar da zaman lafiya da shawo kan kalubale tare domin neman ci gaba na bai daya.

Li Keqiang ya isa Brussels bayan da ya kawo karshen ziyararsa a hukumance a kasar Holland. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China