in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaminstan Sin ya tashi daga Beijing domin fara ziyarar aiki a Tajikistan da Netherlands da Belgium
2018-10-11 15:13:42 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya bar birnin Beijing da sanyin safiyar yau Alhamis, domin halartar taron firaministocin kasashen kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai karo na 17, wanda zai gudana a birnin Dushanbe na kasar Tajikistan.

Firaministan zai kuma gana da shugabannin Tajikistan da Netherlands, bayan haka zai halarci taron hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Turai na ASEM karo na 12, wanda zai gudana a birnin Brussels, yayin da zai gudanar da ziyara a kasar ta Belgium.

Firaministan na Sin zai gudanar da wannan ziyara ne bisa gayyatar firaministan Tajikistan Kohir Rasulzoda, da na Netherlands Mark Rutte, da na Belgian Charles Michel. Sauran su ne shugaban majalissar Turai Donald Tusk, da shugaban hukumar zartaswar kungiyar Jean-Claude Juncker. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China