in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da fashewar bututun mai ya kashe a Najeriya ya kai 24
2018-10-14 16:11:20 cri
Jami'an 'yan sanda a Najeriya sun ce adadin mutanen da suka hallaka a sanadiyyar fashewar bututun mai a karamar hukumar Osisioma dake jahar Abia a kudancin kasar ya kai 24.

Babban jami'in 'yan sandan jahar Abia Anthony Ogbizi, ya ce an sake samun karin mutane 5 da suka mutu wadanda da farko sun tsira da munanan raunukan konar wuta bayan da aka samu fashewar bututun mai a kauyuka biyu dake jahar a ranar Juma'a.

Ogbizi ya dora alhakin fashewar da yoyon da bututun mai ke yi a sakamakon aikin gyaransu da ake gudanarwa a halin yanzu, sai dai ya ce, ana ci gaba da gudanar da karin bincike kan lamarin.

A ranar Juma'a, hukumar tsaron rayukan al'umma ta Civil Defense ta zargi wasu matasan yanki da laifin kwasar man fetur bayan fashewar bututun man.

A 'yan shekarun da suka gabata Najeriya ta sha fama da matsalar yawan fasa bututan mai. Mafi yawa tsagerun yankunan masu albarkatun mai ne ke lalatawa domin kwasar man. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China