in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar adawa ta PDP ta zabi tsohon mataimakin shugaban Najeriya a matsayin dan takarar ta
2018-10-08 09:56:26 cri
A jiya Lahadi ne babbar jam'iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta bayyana tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar, a matsayin dan takarar ta, yayin babban zaben kasar dake tafe a farkon shekara mai zuwa.

Yayin zaben fidda gwani da aka gudanar a daren ranar Asabar, Atiku Abubakar ya doke sauran 'yan takara 11, ciki hadda shugaban majalissar dattawan Najeriya Bukola Saraki, da gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal.

Atiku ya lashe zaben fidda gwanin ne da kuri'u 1,532, wato kusan rabin jimillar kuri'un da aka kada gaba daya, a zaben na birnin Patakwal din jihar Rivers.

Atiku ya rike mukamin mataimakin shugaban Najeriya, tsakanin shekarun 1999 zuwa 2007, ya kuma taba kasancewa daya daga cikin masu marawa gwamnatin dake kan mulki ta shugaban Muhammadu Buhari baya. To sai dai kuma daga baya ya fara sukar gwamnatin mai ci, bayan da ya fice daga jam'iyya mai mulki ta APC cikin shekarar da ta gabata, ya kuma koma jam'iyyar adawa ta PDP. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China