in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta yi hadin gwiwa don bunkasa makamashi ta hanyar tsirrai
2018-10-04 15:21:18 cri
Gwamnatin Najeriya ta ce a shirye take ta yi hadin gwiwa da bangarori masu ruwa da tsaki wajen kara samar da makamashi ta hanyar tsirrai domin inganta tattalin arzikin kasar ta hanyar makamashi mai tsabta, in ji hukumar bunkasa kimiyyar tsirrai ta kasar.

Alex Akpa, mai rikon mukamin babban daraktan hukumar bunkasa kimiyyar tsirrai ta kasar (NABDA) ya fada a Abuja babban birnin kasar cewa, wannan yunkuri ya zama tilas domin cike wagagen gibin da kasar ke da shi na bukatar makamashi.

Akpa, ya bada wannan sanarwa ne a lokacin taron musayar ra'ayoyi game da lalibo damammakin zuba jari a fannin kimiyyar tsirrai da bunkasa ci gaban makamashi ta hanyar tsirrai.

Daraktan ya shedawa mahalarta taron cewa, Najeriya za ta kara zurfafa kokarinta ta hanyar gudanar da bincike kan kimiyyar tsirrai tare da bunkasa ci gaban makamashi ta hanyar tsirrai a kasar.

Ya kara da cewa hukumar ta NABDA ita ce ke da alhakin bunkasa ci gaban kimiyyar tsirrai a Najeriyar, kuma hukumar tana da cibiyoyi 30 a duk fadin kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China