in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mai yiwuwa Najeriya ta fuskanci karancin shinkafa sakamakon ambaliyar ruwa
2018-10-05 15:13:07 cri
Ministan ma'aikatar aikin gona da raya karkara a tarayyar Najeriya Audu Ogbeh, ya ce mai yiwuwa ne a fuskanci karancin shinkafa, sakamakon ambaliyar ruwa da ta lalata gonaki da dama a sassan kasar.

Ministan wanda ya bayyana hakan a ranar Alhamis, yayin zantawar sa da wakilan manoma, ya ce za a iya kaucewa wannan matsala ne kawai, idan aka hanzarta sake shuka sabon iri a gonaki.

Ambaliyar ruwa ta shafi jihohi da dama dake samar da mafi yawan shinkafar da ake nomawa a Najeriya. To sai dai kuma ministan ya ce gwamnati na duba hanyar da za ta bi, domin tallafawa manoman da ambaliyar ruwar ta shafa.

Kaza lika ministan ya ce akwai irin shinkafa da ake samarwa a cibiyar bunkasa irrai ta kasa masu jure ambaliyar ruwa, kamar faro 66, da 67. Don haka ma'aikatar noma ta kasar na fatan gabatarwa manoma irin wadannan nau'o'i na irran shuka a wadace, domin amfani da su a nan gaba. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China