in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang: Sin ta samu ci gaban tattalin arziki a yankunan yammacin kasar
2018-08-23 20:21:56 cri

Firayin ministan kasar Sin, kuma shugaban karamar kungiyar jagorancin aikin raya tattalin arzikin yankunan dake yammacin kasar ta majalisar gudanarwar kasar Sin Li Keqiang, ya kira wani taro a ranar 21 ga watan nan, domin tsarin hanyar gudanar da aikin yadda ya kamata.

Yayin taron, Li ya bayyana cewa, idan ana son kara karfafa gogayya ta samar da kayayyaki a yankunan dake yammacin kasar, ya dace a kara mai da hankali kan sabon tsarin raya tattalin arziki, kana a kara mai da hankali kan aikin bude kofa na yankunan ga sauran yankunan fadin kasar, da kuma kasashen ketare.

Li ya kara da cewa, abu mafi muhimmanci shi ne a ci gaba da nacewa kan manufar yaki da talauci a yankunan, domin kyautata sharadin rayuwar mazauna wuraren, tare kuma da kara samar da aikin yi ga matasa, da kyautata hidimar inshorar ritaya ga tsofaffi.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China