in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasar Habasha sun yi gangami saboda rashin albashi da sauran hakkokinsu
2018-10-11 10:51:27 cri
Daruruwan sojojin kasar Habasha sun yi gangami a jiya Laraba a babban birnin kasar Addis Ababa don nuna bacin ransu sakamakon karancin albashi da sauran hakkokinsu, inda suka toshe hanyar zuwa fadar gwamnatin kasar.

An katse hanyoyin sadarwa na layukan waya da shafukan intanet saboda rudanin da aka shiga a babban birnin kasar.

Firaiministan kasar Abiy Ahmed ya gana da sojojin dake zanga zangar domin sauraron korafe korafensu, kamar yadda kafar yada labaran kasar ta tabbatar da hakan a jiya Laraba.

Zeynu Jemal, shugaban hukumar 'yan sandan kasar Habasha, ya shedawa 'yan jaridu cewa, zanga zangar da sojojin da suka gudanar wanda yawansu ya kai 240 ya haifar da katsewar al'amurra tare da sauran jami'an tsaro dake kusa da fadar gwamnatin kasar.

Da farko dai sojojin masu bore sun bukaci ganin firaiministan kasar ne a yayin da suke dauke da makamai, sai dai daga bisani bayan wata yarjejeniya, an ba su damar ganawa da Ahmed ba tare da makamansu ba, in ji Jemal.

Sojojin Habasha, suna daya daga cikin sojoji mafiya karfi da kuma yawa a nahiyar Afrika, an yabe su da halin nuna da'a, kuma ba kasafai aka fiya jin labarin boren sojojin na kasar ta yammacin Afrika ba, musamman a 'yan shekarun nan. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China