in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kudin shigar da Habasha ke samu daga fitar da kayayyaki daga yankin masana'antu da kasar Sin ta gina ya kai dala miliyan 100
2018-08-31 11:30:07 cri
Habasha ta samu kudin shigar da ya kai dala miliyan 100 daga kayyyakin da ta fitar zuwa ketare a shekarar kudi ta 2017 da 2018 da ya kare a ranar 7 ga watan Yulin da ya gabata. Kasar ta samar da kayayyakin ne daga yankunan masana'antu 6 da kasar Sin ta gina mata.

Da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Kwamishinan kula da harkokin zuba Jari na kasar, Mekuria Belachew, ya ce yankunan 6 da suka dauki ma'aikata 55,000 sun samarwa kasar kudaden da take bukata a cikin shekarar.

Yankunan masana'antun 6 sun hada da Kombolcha da Mekelle da Eastern da Huajian da Hawassa da kuma Modjo.

Kwamishinan ya kara da cewa, ana sa ran Firaministan Habasha Abiy Ahmed, wanda zai kawo ziyara kasar Sin karon farko a makon gobe, don halartar taron dandalin tattaunawar Sin da Afrika, zai ja ra'ayin kamfanonin kasar Sin su zuba jari a bangarorin sarrafa amfanin gona da samar da magunguna na kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China