in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Habasha ya ce takkadamar neman 'yanci da rashin tsari za su iya durkusar da kasar
2018-10-09 10:23:42 cri
Shugaban Habasha Mulatu Teshome, ya ce rikici tsakanin neman 'yanci da rashin tsari na daidaita mutane da haifar da tarin illoli.

Mulatu Teshome, ya bayyana haka ne yayin da ake tsaka da fama da karuwar rikicin kabilanci dake barazana ga sabbin ci gaban da aka samu a kasar dake gabashin Afrika.

A makon da ya gabata ne, ofishin kula da harkokin jin kai na MDD, ya ce sama da mutane 70,000 sun tserewa gidajensu saboda rikicin kabilanci a jihar Benishangul Gumuz dake yammacin kasar.

Hare-hare a karshen watan Satumba ma sun tilatsawa mutane 15,000 tserewa matsugunansu tare da neman mafaka a makarantu da sauran gine-ginen gwamnati a fadin birnin Addis Ababa.

Shugaba Mulatu Teshome, ya yi kira ga al'ummar Habasha da su gujewa dabi'in da ka iya illata kasar. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China