Tawagar dai ta kunshi wakilan kasashen Bolivia da Equatorila Guinea da Faransa. Kasar Bolivia ita ce ke rike da shugabancin kwamitin sulhun majalisar na wannan wata, yayin da kasar Faransa ke zama mambar kwamitin da za ta rubuta shawarwari game da Jamhuriyar demokiradiyar Congo.
A ranar Litinin din mako mai zuwa ne ake sa ran tawagar za ta dawo birin New York na kasar Amurka. (Ibrahim Yaya)