in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe kan iyakokin kasar Kamaru gabanin fara kada kuri'u a babban zaben kasar
2018-10-06 15:07:46 cri
Ministan harkokin cikin gidan kasar Kamaru Paul Atanga Nji, ya tabbatar da rufe kan iyakokin kasar, sa'o'i 48 gabanin fara kada kuri'u a zaben shugaban kasar na gobe Lahadi. Paul Atanga Nji, wanda ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a birnin Yaounde a ranar Juma'a, ya ce za a sake bude kan iyakokin kasar ne kwana guda bayan kammala zaben.

Ministan ya ce mahukuntan kasar sun dauki wannan mataki ne, sakamakon yanayi na zaman dar dar da ake fuskanta a yankunan kasar dake da rinjayen masu magana da Turancin Ingilishi, wadanda ke fafutukar kafa kasar Ambazonia. Tuni dai masu dauke da makamai na wadannan yankuna, suka sha alwashin gurgunta nasarar babban zaben kasar.

Mr. Nji ya kara da cewa, an dakatar da safarar kayayyaki, da mutane a daukacin yankunan ta kasa, da layin dogo, da kuma sama, tun daga karfe 6 na yammacin ranar Asabar din nan 6 ga watan Oktoba, ya zuwa 6 na yammacin ranar Lahadi 7 ga wata. Kaza lika an haramta duk wani taro na jama'a, sai dai fa idan a runfunan zabe ne, inda ake kada kuri'u.

Sama da 'yan kasar miliyan shida da dubu dari biyar ne, ake sa ran za su kada kuri'u a zaben shugaban kasar na gobe, kamar dai yadda hukumar zaben kasar ta tabbatar. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China