in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban CAF ya baiwa Kamaru tabbacin daukar bakuncin gasar AFCON ta 2019
2018-10-03 15:16:50 cri
Shugaban hukumar kwallon kafar nahiyar Afirka (CAF) Ahmad Ahmad ya bayyana a jiya Talata cewa, kasar Kamaru ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin kwallon kafan nahiyar (Afcon) na shekarar 2019. Shugaban ya tabbatar da hakan ne yayin da yake karyata shakkun da wasu ke nunawa game da aniyar kasar ta shirya wannan gasa.

Ahmad ya shaidawa manema labarai bayan ganawarsa da shugaba Paul Biya na kasar Kamaru cewa, hukumar CAF ba ta taba tunanin dauke gasar daga kasar ta Kamaru ba. Tun farko hukumar CAF ta tsara gudanar da gasar ce a kasar Kamaru, amma a makon da ya gabata sai hukumar ta ce za ta duba yadda kasar ta shirya game da daukar bakuncin gasar bayan kammala zaben shugabancin kasar.

Koda ya ke Ahmad ya ce, shawarar daukar bakuncin gasar ko akasin haka ya dogara ne ga kasar ta Kamaru, domin sune za su fada mana cewa sun shirya ko mu kara musu lokaci yanzu ba su shirya ba, domin su ne za su shirya gasar ba hukumar CAF ba.

A baya dai hukumar CAF ta nuna damuwa game da aniyar kasar Kamaru ta shirya gasar, inda ya ba da misali da jinkirin da aka samu wajen gina filayen wasanni da yadda fadan 'yan tawaye masu dauke da makamai ke ci gaba da karuwa a yankunan kasar da ake magana da turancin Ingilshi. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China