in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 17 sun samu raunuka a hadarin gasar tseren kekuna ta kasa da kasa a Kamaru
2018-09-30 16:33:53 cri
A kallla mutane 15 ne suka samu raunuka ciki har da matuka kekuna 15 da wani direba guda 1 da kuma jami'in gasa guda 1 bayan da wata motar bus dauke da 'yan wasan tseren keken na kasa da kasa ta yi hadari, kamar yadda Honore Yossi, shugaban hukumar wasan tseren kekuna na Kamaru ya tabbatar da hakan.

Yossi ya ce, al'amarin ya faru ne da safiyar ranar Asabar a wani waje da ake kira "Memiam" dake babban titin Mbalmayo-Zoetele.

"An kwashe mutanen 17 da suka samu raunuka zuwa wani asibiti dake gundumar Mbalmayo inda aka ba su kulawa karkashin likitoci da ma'aikatan jinyya. Sai dai babu wanda ya mutu daga cikinsu. Mutanen sun samu kananan raunuka ne," in ji Yossi.

Ya ce, hadarin ba zai haifar da cikas game da gudanar da gasar ba.

"Tawagar 'yan wasan daga kasashen Rwanda da Burkina Faso tuni sun riga sun bar asibitin kuma a halin yanzu gab da isa Yaounde. 'Yan kasar Ivorycoast sun yanke shawarar ci gaba da shiga gasar. Raguwar 'yan wasan za su ci gaba da yin gasar," in ji Yossi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China