in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tura dakarun Kamaru zuwa wani Otel mallakar gwamnati gabanin zaben shugaban kasa
2018-09-25 10:48:04 cri
Kasa da makonni biyu kafin zaben shugaban kasa a Kamaru, an yi gaggawar tura dakaru zuwa wani Otel mallakar gwamnatin dake birnin Douala, bayan jin wata kararawar gargadi da babu bukatar ta.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da gwamnan yankin Littoral Ivaha Diboua Samuel Dieudonne ya fitar jiya Litinin.

Wasu ganau a yankin sun ce an tura adadi mai yawa na sojoji da 'yan sanda zuwa Otel din Sawa, bayan an ji karar harbin bindiga a Otel din da yammacin jiyan.

Wani bidiyo da wani ya dauka cikin sirri, ya nuna dakarun bataliyar kai daukin gaggawa suna kwashewa tare da raka fararen hula fita daga Otel din.

'Yan sanda sun yi gaggawar garzayawa wurin tare da rufe shi, sai dai daga baya, Gwamnan ya sanar da cewa an buga kararrawar ne bisa kuskure.

An shiga fargaba a Douala bayan aukuwar lamarin, sai dai Gwamnan ya ce tuni aka dauki matakan da suka dace. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China