in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara yakin neman zaben shugaban kasa a Kamaru
2018-09-23 16:14:37 cri
A jiya Asabar ne aka fara yakin neman zaben shugaban kasa a hukumance a kasar Kamaru, inda 'yan takara guda 9 ke fafatawa don neman lashe kujerar shugabancin kasar.

Za dai a shafe makonni biyu ne a na yakin neman zabe, kafin a kada kuri'a a zaben shugabancin kasar a ranar 7 ga watan Oktoban wannan shekara.

Shugaban kasar mai barin gado Paul Biya kana jagoran jam'iyyar CPDM mai mulkin kasa, yana neman sabon wa'adin mulkin na shekaru 7 da zai ba shi damar kara zama a kan mulkin da ya shafe shekaru 36 a halin yanzu.

Dan takarar babban jam'iyyar adawa ta SDP, Joshua Osih ya kaddamar da yakin neman zabensa ne a Mbanga dake yankin Littotal. Osih dai yana ikirarin kafa tsarin tarayya a kasar ta Kamaru, domin kawo karshen matsalar tsaro da jin dadin jama'a a tsirarun yankunan kasar masu magana da turancin Ingilishi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China