Hua Chunying ta ce, wasu kafofin watsa labarun Amurka, sun rika yada jita jitar cewa, wai Sin ce ta nemi a dage tattaunawar, wanda hakan ya sabawa gaskiyar halin da ake ciki. Ta ce yada wadannan kalamai, na nufin kafofin na da wata boyayyiyar manufa da suke son su cimma, kana hakan ya sabawa hali na gari.
Jami'ar ta kara da cewa, Sin na Allah wadai da wannan zargi, tana kuma fatan sassan dake yada wannan jita jita za su dakatar da aikata hakan. (Saminu Hassan)