Kakakin sashen kula da zirga-zirgar jiragen kasa a lardin Gauteng, Lillian Mofokeng ta ce fasinjoji sun samu raunaka amma ba masu tsanani sosai ba, inda ta ce an kai su asibitocin dake yankin.
A cewarta, wani jirgi da ya samu matsala ne ya karawa wani jirgi dake tsaye.
A nata bangaren, hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasan fasinja ta kasar, ta ce za a gudanar da bincike don gano musababbin hatsarin, tana mai alkawarin yin aiki tare da sauran hukumomi domin nazarin lamarin. (Fa'iza Mustapha)