in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsadar farashin man fetur zai jefa tattalin arzikin Afrika ta kudu da 'yan kasar cikin garari: Masana
2018-10-03 16:02:49 cri
Masana sun yi gargadin cewa tsawwala farashin man fetur a kasar Afrika ta kudu zai iya haifar da gagarumar illa ga tattalin arzikin kasar, da haifar da tsadar kudaden tafiyar da harkokin kasuwanci da rage kudaden shigar masu sayayyar kayayyaki a kasar.

Sashen kula da makamashin kasar ne ya sanar a wannan makon cewa, farashin man fetur a kasar zai karu da kashi 99 bisa 100 wato daga Rand 1.24 a kan kowace lita tun daga yau Laraba. A wasu lardunan kasar masu ababen hawa za su dinga biyan Rand 17.08 a kan kowace litar man fetur.

Wannan shi ne karo na 7 da aka kara farashin mai a kasar cikin shekarar nan ta 2018. Sakamakon faduwar darajar kudin kasar Rand, da tashin farashin mai a kasuwannin duniya na daga cikin dalilan da suka haifar da kara farashin kudin man fetur din a Afrika ta kudu.

Wani masanin tattalin arziki na hukumar Efficient Group, Dawie Roodt, ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a jiya Talata cewa, karin farashin man fetur na baya bayan nan zai haifarwa mafi yawan masu sayan kayayyaki a kasar raguwar kudaden shigarsu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China