A kokarin rage fargabar da ake yi game da kudurin gwamnatin na karbar filaye ba tare da biyan diyya ba, Shugaba Ramaphosa ya ce 'yan kasar manoma bakaken fata, sun samu damar noma, don tabbatar da wadatar abinci da samun abun yi.
Shugban na wannan jawabi ne a wajen wani taro da Kungiyar Manoman Afrika reshen Afrika ta kudu ta shirya a Kempton dake lardin Gauteng, wanda ya mayar da hankali kan tabbatar da bakaken fata suna shiga ana damawa da su cikin hada-hadar kasuwancin a bangaren aikin gona. (Fa'iza Mustapha)