in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Afrika ta Kudu zai yi bayani game da manufar kasarsa ta sauya tsarin mallakar filaye ga babban zauren MDD
2018-09-24 15:40:00 cri
Shugaba Cyril Ramaphosa na Afrika ta Kudu, zai yi amfani da taron babban zauren MDD dake karatowa, wajen yin bayani game da manufar gwamnatinsa ta sauya tsarin mallakar filaye, wadda ake ta tafka muhawara kanta a ciki da wajen kasar.

Yayin da Cyril Ramaphosa ya isa birnin New York don halartar taron zauren MDD karo na 73, fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta ce ana sa ran shugaban zai jaddada cewa, sauya tsarin mallakar filaye da Gwamnatinsa ta mayar da hankali kai, na da nufin inganta zaman lafiya da tafiya tare dukkan al'umma da kuma sauya tsarin tattalin arzikin kasar.

Taron na bana zai zama karon farko da Cyril Ramaphosa zai halarta a matsayin shugaban kasa.

Za kuma a dama da shi cikin muhawarar da ake yi duk shekara, inda shugabannin kasashen duniya ke haduwa a hedkwatar MDD domin tattauna batutuwan da suka shafi duniya baki daya.

Tun da Cyril Ramaphosa ya kama aiki a watan Fabrerun bana, Gwamnatin Afrika ta Kudu ta fara gaggauta aiwatar da shirin na sauya tsarin mallakar filaye, wanda ya kunshi kwace filaye ba tare da biyan diyya ba, abun da ya haifar da damuwa a ciki da wajen kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China