in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya lashi takobin 'yantar da 'yan matan Sakandare dake hannu Boko Haram
2018-10-04 15:08:44 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta yi dukkan mai yuwuwa, don ganin ta karbo dalibar nan Leah Sharibu da Boko Haram ta sace.

Leah Sharibu ita kadai ta rage a hannu kungiyar Boko Haram, kana ita ce kadai Kirista cikin dalibai 'yan mata 110 na Sakandaren 'yan mata ta gwamnati dake garin Dapchin jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar, da kungiyar ta sace.

Muhammadu Buhari, ya wallafa jiya a shafinsa na Twitter cewa, ya yi magana da Rebecca Sharibu, mahaifiyar Leah, kuma ya tabbatar mata cewa gwamnati za ta dawo mata da 'yarta lafiya.

Ya ce addu'o'in 'yan Nijeriya na tare da iyalan gidan Sharibu, da ma sauran iyalan wadanda har yanzu suke hannun kungiyar. Yana mai cewa za su yi dukkan abun da za su iya don ganin sun 'yantar da su.

Rahotanni na cewa, wani tsagi na kungiyar Boko Haram ya ba gwamnatin kasar wa'adi zuwa ranar 15 ga wannan watan, don ta biya bukatar da ya gabatar mata game da sakin Leah ko kuma su kashe ta. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China