in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ce ke kan gaba a yawan masu fita ketare don yawon bude ido
2018-10-04 15:47:09 cri

Hukumar kiddidiga ta kasar Sin, ta ce kasar ce ke da mafi yawan adadin masu fita kasashen ketare domin yawon bude ido.

Idan aka kwanta da miliyan 5 na shekarar 1995, kiddidiga ta nuna cewa, adadin tafiye-tafiye da Sinawa suka yi zuwa wasu kasashe a shekarar 2016 ya kai miliyan 135.

Wannan ya nuna cewa ana samun karuwar kaso 17.6 a kowace shekara cikin shekaru 21 da suka gabata.

Hukumar ta ce a kowace shekara tun daga 2013, kasar Sin ce ke kan gaba a yawan masu zuwa kasashen ketare domin yawon bude ido. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China